25/07/2022
Uwa Ta Gari
Kashi Na 1
Abu Na Farko 'Yan Uwa Muyi Koƙari, Manufar Da ALLAH Ya Shar'anta Mana Addini Shine Domin Mu Samu Tsira
Dama Ce Babba A Rayuwa ALLAH Ya Fahimtar Dakai Addini, ALLAH Ya Soyantar Maka Da Imani, ALLAH Ya Ƙyamatar Maka Da Kafirci Da Saɓon ALLAH
Yana Daga Cikin Manya Manyan Ni'imomi Da ALLAH Kema Bawa, Shine Ya Buɗe Zuciyar Sa Bawan Yazam Bawane Mai Karɓan Canji A Rayuwar Sa
Duk Lokacin Da Yaga Abun Da Ba Daidai Ba Zai Dawo Kan Abinda Yake Daidai, Muyi Ƙoƙari Mu Ribaci Wannan Dama Ta Rayuwa Da Lafiya Da Imani Da ALLAH Subhanahu Wata'ala Ya Azurtamu Dashi
Akwan A Tashi Wataran Za'a Wayi Gari Bama Nan 😓
Abunda Muka Karanta Ko Abinda Mukaji Ankaranta Mukayi Aiki Dashi, Jama'a Shine Zai Amfane Mu
Annabi ﷺ Yace; Abubuwa Guda Uku Suke Rakiya Wa Ɗan Adam Bayan Ya Mutu, Dukiyar Sa Zata Mai Rakiya Wataƙil Lokacin Daza'a Kai Ka Maƙabarta Atafi Harda Motar Ka Annabi Yace;Dukiyarka Zata Ma Rakiya, Iyalan Ka Zasu Ma Rakiya, Annabi Yace; Ayyukan Ka Suma Zasu Bika Maƙabarta 😓
Annabi ﷺ Yace; Biyu Zasu Dawo Su Bar Ɗaya Tare Dakai, Da Dukiyarka Da Iyalanka Zasu Dawo Iyalankan Su Raba Gadon Dukiyarka
Amma Zasu Bar Ka Da Aikin Ka Dashi Daka Ƙare Zaman Ka Acikin Kabari Aje A Maka Hisabi Dashi Abaka Makomar Ka.
Mu Haɗu A Kashi Na Gaba 🙏
Ku Tayamu Da Addu'a Na Fatan Alkairi 'Yan Uwa