17/07/2026
GIDAN GWAMNATIN JIHAR BAUCHI
SANARWAR MANEMA LABARAI
GWAMNA BALA MOHAMMED YA AMINCE DA ƘANANAN SAUYE-SAUKYE A MAJALISAR ZARTASWA TA JIHAR
Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, CON, FNIPR (Kauran Daular Usmaniyya), ya amince da yin wasu ƙananan sauye-sauye a cikin Majalisar Zartaswa ta Jihar a matsayin wani ɓangare na ci gaba da ƙoƙarin gwamnatinsa na ƙarfafa shugabanci da inganta ayyukan yi wa al'umma hidima a faɗin jihar.
A cikin sauye-sauyen, Kwamishinan Kasuwanci, Masana'antu da Zuba Jari, Alhaji Mohammed Salis Gamawa, da tsohon Kwamishinan Ilimi wanda daga bisani aka mayar da shi Ma'aikatar Wutar Lantarki, Kimiyya da Fasaha, Dr. Mohammed Lawal Rimin Zayam, sun fita daga Majalisar Zartaswar Jihar nan take. Haka kuma, Gwamnan ya amince da murabus ɗin tsohon Kwamishinan Raya Karkara da Harkoki na Musamman, Hon. Faruk Mustapha.
Domin tabbatar da ci gaba da ingantaccen gudanar da mulki ba tare da tangarɗa ba, an miƙa sunayen waɗanda aka zaɓa domin maye gurbinsu, tare da sauran waɗanda aka tsayar domin cike guraben da s**a samu sakamakon ficewar wasu kwamishinoni a baya, zuwa Majalisar Dokokin Jihar Bauchi domin tantancewa da amincewa.
Gwamna Bala Mohammed ya bayyana matuƙar godiya ga kwamishinonin da s**a bar muƙamansu bisa sadaukarwa, jajircewa, da gudunmawar da s**a bayar wajen ci gaban Jihar Bauchi a lokacin da s**a yi aiki. Ya yi musu fatan alheri da nasara a rayuwarsu ta gaba, tare da jaddada aniyar gwamnatinsa na ci gaba da gina gwamnati mai inganci, mai sauraron jama'a, kuma mai samar da kyakkyawan sakamako domin amfanin al'ummar Jihar Bauchi.
Mai Sa Hannu:
Mukhtar Gidado, MNIPR
Mai Bai Wa Gwamna Shawara Na Musamman kan Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama'a
17 ga Yuli, 2026.