26/01/2023
Koyi da Maulana Prof. Ibrahim Maqary 001
Wata rana wata mata wacce mukayi sanadin haɗuwa da ita anan facebook ɗin.
Mun saba da juna sosai amma babba ce dan ta kusa haihuwata.
Sai take bani labarin cewa tana da ƙawa amma ƙawar tana buƙatar taimako domin da ƙawar taɗin ba musulma bace, sai ta haɗu da wani soja musulmi ya aure ta ya kuma musuluntar da ita, bayan sun kai shekaru 20 da aure, sai Allah yayi ma sojan rasuwa a Maiduguri sanadin yaƙi bayan ya rasu to dama ƙawar tata ɗin ita kaɗai ce musulma a gidan kuma sanadin mijin nata ne ta musulunta ta watsar da danginta gaba ɗaya ta zaɓi musulunci da mijin nata.
Bayan tsawon lokacin da s**a ƙwashe a tare gashi kuma ta saba da musulunci ta haifi ƴaƴa kusan biyar a cikin musulunci kuma duk musulmai ga kuma miji ya rasu sai ta dawo gida inda danginta suke s**aƙi amsarta s**a watsar da ita to da yake aƙwai wani abu da ake bayarwa na kuɗin makarantar yara sai take amfani dashi har ya ƙare amma ko wata uku bayayi mata a cikin watanni sha biyu kuma duk shekara ake badawa, sai baiwar Allahn nan ta kasa haƙuri ta koma gurin ƴan uwanta sai s**a amsheta amma da sharaɗin zata koma Kiristancinta, sai kuwa ta amince saboda tsananin wahalar da take sha kota fara sana'a bata ɗorewa ga kuɗin makarantar yara ga abinci ga haya da sauran matsalolin rayuwa.
Bayan ta shafe lokaci a cikin Kiristancin sai taji gaskiya bazata iya zama ba, sai ta zaɓi ta fita kiristancin to amma babu mai taimakonta kota koma musulunci domin ta nemi ƙungiyoyi da dama an haɗata da limamai da sauran ƙungiyoyi na addini shuru sun ƙyaleta shi yasa ma ta koma kiristancin da musulmai sun kawo mata ɗauki da bazata koma kiristancin ba.
Sai wannan matar dana haɗu da ita anan facebook ta nemi na haɗata da Prof. Ibrahim Maqary, ya musuluntar da ita kuma ya taimaketa, bayan mun gama magana sai na samu wani bawan Allah ya bata dubu goma ta hau mota daga Sokoto zuwa Abuja bayan ta sauka kuɗi ya ƙare muka samu wasu kuɗi na zirga zirga da abinci muka ƙara tura mata taje gurin Prof. sai a zuwa na biyu s**a haɗu bayan sun haɗu dashi sai ta karanta mishi matsalarta dama nima nayi masa bayani.
Matsalolinta uku ne
1. Tanason ta koma Musulunci.
2. Tana neman taimakon kuɗin da zata biya ma babban ɗanta registration na Poly a Sokoto ya samu admission
3. Kuɗin da zata riƙe a hannu ta riƙa kashewa da abinci da biyan kuɗin makarantar sauran yara da sauran abubuwa.
4. A aurar da ita.
Bayan Maulana yaji matsalolinta, sai yace ta kawo takardun yaron ya sanya shi a Private University, Abuja. Ba kuɗin registration ɗin Poly zai bata ba University ta kuɗi zai sanya shi fa yace.
Ya kuma ce zai musuluntar da ita zai mata aure kuma zai bata abinda zata riƙe a hannunta.
Kaɗan daga cikin abubuwan da Maulana yakeyi kenan fa dan ni kaina na kai mutane sunfi biyar da kusan irin wannan matsalolin
Dalilin wannan dogon rubutun shine:
Yanzu da ace munada irin wannan gidauniyar da muke ƙoƙarin assasawa a yanzu da bazamu tura irin wannan matar gurin Maulana ɗin ba, da sauran makamantan irinsu dama ƴan ƙananun abubuwa waɗanda bazamu iya ba sai a ƙungiyance sannan kuma tunatawar ne akan duk mai cewa yanason Maulana to ba a baki zai bar abin ba a aikace zaiyi domin shima idan ya faɗa yana aikatawa ne ba yana jiran sai ya samu ba, ni nasan lokacin da Maulana sai dai yayi alƙawari ya jira sai kuɗi sunzo sannan yayi wallahi sau da yawa zaiyi ma mutanen dake neman taimako alƙawari kuma bashi da kuɗi a lokacin da kuɗi sun shiga kuma zai cika alƙawarin abubuwa sunyi masa yawa ne matuƙa.
Mu daure mu assasa wata gidauniya da sunan koyan sunnarsa domin faranta ma mabuƙata kamar yadda yanzu haka muka fara kuma da izininsa.
Muna da kuɗi Naira 6000 a account ɗinmu kuma zamu buɗe account na gidauniyar tamu da zarar komai ya lafa na sha'anin canjin kuɗin nan da akeyi.
Zaka iya saka naka tallafin a 👇
3101004274
First Bank
Anas Usman
Allah yasa mu dace ya ƙarama Maulana lafiya ya kuma bamu ikon yin koyi dashi da ƙyaƙƙyawar niyyah