Tauraruwa Hausa

Tauraruwa Hausa Actor

Da Dumi-Dumi: Matashin Da Ya Fi Kowa Taimakon Talakawa a Kano, Fahad Ɗan Kabo, Ya Yanki Fom ɗin Takarar Dan MajalisaFita...
02/05/2026

Da Dumi-Dumi: Matashin Da Ya Fi Kowa Taimakon Talakawa a Kano, Fahad Ɗan Kabo, Ya Yanki Fom ɗin Takarar Dan Majalisa

Fitaccen matashin ɗan siyasa, Fahad Ɗan Kabo, wanda aka fi sani da jajircewarsa wajen taimakon talakawa da tallafa wa al’ummar Jihar Kano ta fannoni daban-daban, ya yanki fom ɗin takarar ɗan majalisar tarayya Kabo da Gwarzo

Fahad Ɗan Kabo, ɗa ga ɗaya daga cikin manyan attajiran Jihar Kano, Alhaji Ɗan Adamu Kabo, ya shahara wajen gudanar da ayyukan alhairi da s**a haɗa da tallafa wa marasa galihu, bayar da tallafin karatu ga ɗalibai, taimaka wa matasa wajen dogaro da kai, da kuma kai ɗauki ga mabukata a lokuta daban-daban.

Matakin da ya ɗauka na shiga wannan takara ya haifar da farin ciki da fatan alheri a tsakanin al’ummar Kano, inda da dama ke bayyana shi a matsayin matashi mai kishin jama’a, hangen nesa da kuma ƙudirin kawo ci gaba mai ma’ana.

Mutane da dama na ganin shigowarsa siyasa a wannan mataki wata babbar dama ce ga al’ummar Kano domin samun wakilci nagari daga matashi mai tausayi, kishin talakawa da kuma burin inganta rayuwar jama’a.

Hon. Dauda Dalladi Mahuta ya bayyana alhini da jimami bisa rasuwar Hajiya Hauwa (Maijeddah), uwargidan Shugaban Ma’aikat...
16/04/2026

Hon. Dauda Dalladi Mahuta ya bayyana alhini da jimami bisa rasuwar Hajiya Hauwa (Maijeddah), uwargidan Shugaban Ma’aikatan Gidan Gwamnatin Jihar Katsina, Hon. Abdulƙadir Mamman Nasir Andaje.

Tsohon Sakataren Mulki A Ƙaramar Hukumar Dandume Jihar Katsina Hon. Dauda Dalladi Mahuta ya mika sakon ta’aziyyarsa ga Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, da iyalan marigayiyar, tare da daukacin al’ummar Jihar Katsina bisa wannan babban rashi da ya girgiza zukata.

Hon. Dauda Ya bayyana marigayiyar a matsayin mace ta gari mai kyawawan halaye, wadda ta rayu cikin mutunci da hidima ga iyali da al’umma. Ya ce rasuwarta babban gibi ne da za a dade ana jin irinsa.

Hon. Dauda Dalladi Mahuta ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki da Ya jikanta da rahama, Ya gafarta mata kura-kuranta, Ya sa Aljannatul Firdausi ta zamo makomarta. Haka kuma, Ya bai wa iyalanta da daukacin al’umma haƙurin jure wannan rashi.

“Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un.”

HON. BASIRU MUSA YA AIKA SAƘON BARKA DA SALLAH GA GWAMNA DIKKO RADDA, ____Yayi Kira Da Haɗin Kai Da Sake Goya Bayan Gwam...
22/03/2026

HON. BASIRU MUSA YA AIKA SAƘON BARKA DA SALLAH GA GWAMNA DIKKO RADDA,

____Yayi Kira Da Haɗin Kai Da Sake Goya Bayan Gwamantin Malam Dikko Radda Karo Na Biyu.

Mataimakin Shugaban Karamar Hukumar Dandume, Hon. Basiru Musa, ya mika sakon taya murna da fatan alkhairi ga Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda PhD. CPN, bisa zagayowar bikin Sallah.

A cikin sakon nasa, Hon. Basiru Musa ya bayyana Sallah a matsayin lokaci na godiya ga Allah Madaukakin Sarki, tare da tunatar da al’umma muhimmancin hakuri, tausayi, da taimakon juna, musamman ga marasa galihu a cikin al’umma.

Ya kuma yi kira ga jama’ar Karamar Hukumar Dandume da daukacin al’ummar Jihar Katsina da su kara hada kai da juna, su zauna lafiya, tare da ci gaba da bayar da goyon baya ga manufofi da shirye-shiryen gwamnatin Malam Dikko Umar Raɗda, domin samun ci gaba mai dorewa.

Hon. Basiru Musa ya jinjina wa kokarin Gwamna Radda wajen tabbatar da tsaro, bunkasa tattalin arziki, da inganta rayuwar al’umma, yana mai cewa irin wadannan tsare-tsare ne ke kawo sauyi mai ma’ana a rayuwar talakawa.

A karshe, ya yi addu’ar Allah Ya karbi ibadun al’ummar Musulmi, Ya maimaita mana wannan lokaci cikin koshin lafiya da zaman lafiya, tare da kara dankon zumunci a tsakanin al’umma.

Barka da Sallah!

22/03/2026

HON. DAUDA DALLADI MAHUTA YA AIKA SAƘON BARKA DA SALLAH GA SANATA DANDUTSE DA ALHAJI ABDULLAHI ALBASU.

Tsohon Sakataren Ƙaramar HukumaR Dandume a Jihar Katsina, kuma mai riƙe da muƙamin kansila mai ofis "Supervisior Cancilor" a halin yanzu, Hon. Dauda Dalladi Mahuta, ya miƙa saƙon taya murna ga al’ummar Musulmi, musamman ga Sanatan Shiyyar Funtua, Muntari Mohammed Dandutse, da kuma Shugaban Rukunin Kamfanonin A.A Albasu Nigeria Limited, Abdullahi Albasu, bisa zagayowar bikin Ƙaramar Sallah.

A cikin saƙon nasa, Hon. Mahuta ya bayyana Sallah a matsayin wata babbar dama ta ƙarfafa zumunci, haɓaka haɗin kai, da kuma ci gaba da nuna tausayi da jinkai a tsakanin al’umma.

Ya yaba da irin gudunmawar da Sanata Dandutse ke bayarwa wajen wakiltar al’ummar Shiyyar Funtua, tare da ƙoƙarin kawo ci gaba a fannoni daban-daban, musamman a bangaren walwala da jin daɗin jama’a.

Haka zalika, ya jinjinawa Alhaji Abdullahi Albasu bisa rawar da yake takawa a fannin kasuwanci da samar da ayyukan yi, wanda a cewarsa yana taimakawa matuƙa wajen bunƙasa tattalin arziki da rage zaman kashe wando a tsakanin matasa.

Hon. Mahuta ya ƙara da cewa, lokaci ne da ya kamata a ci gaba da riƙo da darussan watan Ramadan, musamman haƙuri, juriya, da taimakon juna, domin gina al’umma mai cike da zaman lafiya da ci gaba.

A ƙarshe, ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki da Ya karɓi ibadun al’ummar Musulmi, Ya kuma maimaita wannan lokaci cikin ƙoshin lafiya, zaman lafiya da wadata.

Allah Ya maimaita mana da alkhairi.

SAKON FATAN ALHERI DA BARKA SALLAH GA GWAMNA DIKKO RAƊƊA.Daga: Hon. Dauda Dalladi Mahuta.An bayyana sakon fatan alheri d...
20/03/2026

SAKON FATAN ALHERI DA BARKA SALLAH GA GWAMNA DIKKO RAƊƊA.

Daga: Hon. Dauda Dalladi Mahuta.

An bayyana sakon fatan alheri da taya murna barka da idin karamar sallah ga Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Umar Dikko Radda PhD. CON, a yayin da al’ummar Musulmi duniya ke gudanar da bukukuwan karamar Sallah na shekarar 1447AH (2026).

Honarabul Dauda Dalladi Mahuta, kansila mai ofis a karamar hukumar Dandume, ya aike da wannan sakon ne domin nuna goyon baya, girmamawa da kuma jinjinawa irin kokarin da Gwamna Radda ke yi wajen tafiyar da harkokin mulki cikin adalci da gaskiya, tare da kokarin bunkasa ci gaban jihar Katsina a fannoni daban-daban.

A cikin sakon, ya yi addu’ar Allah ya kara wa Gwamnan lafiya, basira da hikima wajen sauke nauyin da ke kansa, tare da rokon Allah ya sanya wannan Sallah ta zo da zaman lafiya, hadin kai da wadata ga al’ummar jihar Katsina da kasa baki daya.

Hakazalika, ya bukaci al’umma da su ci gaba da bai wa gwamnati goyon baya da hadin kai domin tabbatar da dorewar zaman lafiya da ci gaba mai dorewa.

A karshe, Hon. Dauda Dalladi ya taya daukacin al’ummar Musulmi murnar zagayowar wannan babbar rana ta Sallah, yana mai fatan Allah ya karbi ibadu da addu’o’insu.

G.M Usman Rabi'u Mahuta Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Azumin Watan Ramadan Ga Marasa Karfi, Wanda Ya Hada Da Shinkafa, Gero...
01/03/2026

G.M Usman Rabi'u Mahuta Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Azumin Watan Ramadan Ga Marasa Karfi, Wanda Ya Hada Da Shinkafa, Gero, Masara Kimani Buhu 5000.

Shugaban gidauniyar (U.R.M Foundation) kuma babban manaja na kamafanin (Blue Camel Nigeria Limited) reshen jihar Katsina, G.M Usman Rabi'u Mahuta (Talban Dandume), ya kaddamar da rabon tallafin kayan azumin watan ramadan ga marassa karfi da masu bukata ta musamman, da shugabannin Jam'iyyar APC, wanda ya hada da Shinkafa buhu 1500 mai nauyi 45kg, Masara buhu 1500 mai nauyi 10kg Gero buhu 2000 mai nauyin 10kg.

An gudanar da bikin kaddamarwar ne a harabar makarantar firamaren garin Mahuta karamar hukumar Dandume jihar katsina a ranar Asabar 28 ga watan fabrairu, 2026.

A jawabin Mai garin mahuta Malam Sani Hamza ya yabawa mai girma gwamna Malam Dikko Umar Radda Phd, CON akan irin ayyukan da yake yi na raya kasa da kuma gina al'umma tun daga matakin akwatin zabe har zuwa matakin jiha babu inda aikin shi bai kaiba, ya kuma yi godiya da G.M Usman Mahuta akan irin yadda yake taimakon al'umma babu dare babu rana daga karshe ya rufe jawabin shi da zayyano kadan daga cikin ayyukan da gidauniyar tayi a fadin karamar hukumar Dandume irin su ayyukan raya kasa da kuma gina al'umma, taimakon marayu tare da marassa karfi.

Shi kuwa Kansilan Dantankari Hon. Salisu K.K fatan alkhairi yayi ga G.M, ya kuma yi kira ga sauran al'umma da suyi koyi da halin G.M.

A na shi jawabin shugaban jam'iyyar APC na karamar hukumar Dandume Hon. Shafi'u Lawal Dantankari, Ya bayyana irin yadda G.M yake nuna kishin shi akan al'ummar karamar hukumar Dandume dama jiha baki daya, ya kuma yabawa Malam Dikko Umar Radda akan irin yadda ya ba sashen kiwon lafiya muhimmanci tun daga matakin kanannan asibitoci har zuwa manya da kuma yadda yake kokari wajen ganin an samu zaman lafiya a jihar katsina, ya kuma roki maigirma gwamna da ya kara rike masu G.M da kyau sakamakon mutum ne mai kishin al'ummar shi.

A nashi bangaren Wakilin matasan karamar hukumar Dandume, ya yabawa Talban akan irin kokarin da yake yi na tallafawa marasa karfi da marayu, ya kuma yi kira ga shugabanni da suyi adalci a tsakanin al'umma domin shugabanci abune mai wahala, ya taya sabon shugaban jam'iyyar karamar hukumar, ya kuma yabawa gwamna akan irin yadda yake kishin al'ummar katsina ta kudu dama jiha baki daya.

A jawabin Uban Taro G.M Usman Rabi'u, ya bayyana irin farin cikin shi da allah ya nuna mashi wannan rana da zai kaddamar da kayan azumi ga marassar karfi, ya kuma bayyana irin yadda ya ke yin ayyukan alkhairi akaramar hukumar ddm dukkananin abinda yake bayar wa na tallafi baya nuna banbanci a tsakanin al'umma.

Ya kuma bayyana irin yadda kan 'yan siyasar karamar hukumar Dandume ya ke a hade, bayan haka ya yi kira ga matasa da suyi koyi da ayyukan alkhairi kuma su rika yi ma kansu hisabi, ya kuma kara kira ga sauran al'umma akan ko yaya mutum ya samu dama ko ya take to yayi kokari ya tallafawa wanda baida shi.

Bayan haka ya kuma sake wani kiran ga matasa da su cire tsoro su shigo cikin siyasa adama da su, ya kuma fadi cewa "ko dan gidan mu ne kai idan baka son malam Dikko Radda to muma bamuson ka koda kuwa dan gidanmu ne kai", daga karshe ya rufe bayanin shi da kira ga matasa da su daina bangar siyasa.

Taron yasamu halartar Shugaban karamar hukumar Dandume, Shugabannin jam'iyyar Apc na karamar hukumar hukumar Dandume Alhaji Shafi'u Dantankari, wakilin katukan Katsina hakimin Dandume Shamsu Ibrahim Sambo, tsofaffafin shugabannin jama'iyyar Apc, sauran al'ummar gari maza da mata, jami'an tsaro, yan jarida.

Hotuna: Karaduwa Post

Dukkanin mazaɓu a Karamar Hukumar Dandume da ke Jihar Katsina sun amfana da tallafin kayan abincin azumin watan Ramadan ...
24/02/2026

Dukkanin mazaɓu a Karamar Hukumar Dandume da ke Jihar Katsina sun amfana da tallafin kayan abincin azumin watan Ramadan daga gidauniyar 'Tafidan Dandume Foundation'.

Ana ci gaba da rabon buhunan kayan abinci guda ashirin ga kowace mazaɓa, inda kowane buhu ke ɗauke da kilo 10 na masara, gero da sauran kayan abinci. Haka kuma an ware tallafi na musamman ga kungiyoyin al’umma daban-daban a ranar Talata, 24 ga Fabrairu, 2026.

Tallafin ya fito ne daga fitaccen matashi masanin harkokin noma a Arewacin Najeriya, Alhaji Ibrahim Shu'aibu (Tafidan Dandume), wanda shi ne Shugaban kamfanin (Shiagro Nigeria Limited) kuma jagoran kungiyar (Tafida Youth Organization For Dikko 2x).

Za a rabawa shugabannin jam’iyyar APC, matasa, kungiyoyin ’yan kasuwa da al’ummar Musulmi kayan tallafin domin sauƙaƙa musu yayin azumin watan Ramadan mai alfarma. An ƙaddamar da shirin ne a ma’ajiyar kayan abinci da ke garin Zaria a ranar Lahadi, 22 ga Fabrairu, 2026.

A cewarsa, an ware tallafin ne domin rage raɗaɗin halin da jama’a ke ciki a wannan lokaci na azumi, tare da fatan samun zaman lafiya a Najeriya baki ɗaya. Ya kuma yi kira ga al’ummar Musulmi da su ƙara dagewa da addu’o’in samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a ƙasa.

~Karaduwa Post

Hon. Dauda Dalladi Mahuta Ya Mika Sakon Bangajiya Ga Malam Dikko Radda Bayan  Kaddamar Da Tallafin Azumin Watan Ramadan ...
17/02/2026

Hon. Dauda Dalladi Mahuta Ya Mika Sakon Bangajiya Ga Malam Dikko Radda Bayan Kaddamar Da Tallafin Azumin Watan Ramadan Na Sanata Muntari Dandutse.

"Sanata Muntari Dandutse Zama Daram-Dam, Domin Ina Tabbatar Maka, Ina Tabbatar Ma Mutanen Wannan Yankin, Ina Bayanka" Inji- Gwamna Radda

Tsohon sakataren mulki na karamar hukumar Dandume jihar katsina Hon. Dauda Ɗalladi kuma Kansila mai ofis a yanzu ya mika sakon bangajiya ga maigirma gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umar Raɗɗa PhD. CON. Bisaga halaktar taron ƙaddamar da tallafin kayan Azumin Watan Ramadan mai albarka na kimanin zunzurutun ƙudi Naira miliyan dari uku da dubu dari bakwai da sha ɗaya N346,711,000, Wanda ɗan majalisar dattawan mai wakiltar shiyyar Katsina ta kudu (Funtua zone) jihar katsina, Sanata Muntari Muhammad Dandutse, Ya masar ga al'ummar shiyyar, wanda ya saba yi duk shekara.

An gudanar da taron ne a dakin ajiye kaya na Dandutse store dake kan titin bypass cikin garin Funtua, a ranar lahadi 15 ga watan Fabrairu, 2026.

Maigirma gwamnan jihar katsina Malam Dikko Umar Radda PhD, CON, ya bayyana farin cikin shi da Allah ya nuna mashi wannan rana, gwamna Radda ya yabawa Sanata Dandutse akan irin yadda yake kishin shiyyar funtuwa da kuma jihar katsina baki daya, ya kuma kira ga shugabanni da 'yan kasuwa suji tsoron Allah su tausayawa tallakawa musamman a wannan watan da yake tunkaro mu na ramadan, ya tabbatar wa al'ummar jihar katsina za'a ci gaba da ayyukan alkhairi.

"Sanata Muntari Dandutse Zama Daram-Dam, Domin Ina Tabbatar Maka, Ina Tabbatar Ma Mutanen Wannan Yankin, Ina Bayanka" Inji- Gwamna Malam Dikko Radda

"Ina Bayan Mutumin Da Ke Taimakon Al'umma, Ina Bayan Mutumin Dake Taimakon Jam'iyya, Ina Bayan Mutumin Dake Tausayin Takakawa" inji Radda.

Dauda Ɗalladi, ya bayyana wannan a matsayin abin ayaba yadda gwamnan jihar Katsina ya yi babban karamachi ga sanata Muntari Dandutse, daga karshe yayi addu'ar samun nasarar jam'iyyar APC a zaben shekara 2027.

11/02/2026

BIDIYO 🎥Yadda Shugaban APC na Ƙasa Ya Kaddamar da Motoci 5 da Hon. Ibrahim Shuaibu Ya Bayar Gudunmawa Ga Gwamnatin Katsina, Domin Cigaba Da Gudanar Ayyukan Jam'iyya.

Gwamna Radda Ya Kai Ziyarar Girmamawa ga His Excellency sah Hamisu Kero Dandume Ɗan Kasuwa Ɗan Asalin Jihar Katsina A Bi...
09/02/2026

Gwamna Radda Ya Kai Ziyarar Girmamawa ga His Excellency sah Hamisu Kero Dandume Ɗan Kasuwa Ɗan Asalin Jihar Katsina A Birnin Abuja.

Fitaccen ɗan kasuwa ɗan asalin karamar hukumar Ɗandume jihar Katsina His Excellency Isah Hamisu Kero Dandume, Manajan Darakta kuma Babban Jami’in Gudanarwa (MD/CEO) Na Rukunin kamfanonin 'Abuja Gold and Silver Intl. Limited' kuma jakadan Renewed Hope na Ƙaramar Hukumar Dandume, Ya karɓi bakuncin mai girma gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, CON, ziyarar girmamawa da sada zumunci ofishin sa dake Wuse II birnin tarayyar Najeriya Abuja.

Ziyarar ta gudana cikin yanayi na girmamawa da ƙarfafa zumunci, inda aka tattaunawa muhimman batutuwan da s**a shafi ci gaban al’umma da ƙasa baki ɗaya, da kuma hanyoyin ƙarfafa haɗin kai domin cimma muradun jama’a.

Isah Kero yana taka muhimmiyar rawa wajen haɗa kai da bunƙasa al’umma, An bayyana fatan cewa ziyarar za ta ƙara dankon zumunci da haɗin kai tsakanin bangarorin biyu, tare da bayar da gudummawa mai ma’ana ga ayyukan hidimtawa al’umma.

Karaduwa Post
09/02/2026

Address

Kaduna

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Tauraruwa Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share