16/08/2025
MULKIN ADALCI Manzon Allah SAW Yace" Ba Cuta Ba Cutarwa" A lokacin Khalifancin Sayyadina Umar bn Khattab (RA), ya kasance yana yawo tsakiyar dare a cikin garin Madina domin ganin halin da jama'ar Madina ke ciki.
Sai Wata rana suna cikin zagaya garin Madina sai s**a ji ƙarar yara suna kuka a cikin wani gida.
Sayyidina Umar (RA) ya matsa kusa da gidan, ya nemi izini shiga gidan domin ya duba abin da ke faruwa.
Sayyidina Sai ya tarar da wata mata ta dora tukunya a kan wuta, yayin da yaranta ke kuka suna jiran abinci. Sai Khalifa Umar ya tambaye ta:
"Me k**e dafa wa haka, kuma me yasa yara ke kuka?"
Sai matar ta ce:
"Babu abinci a cikin tukunyar, ruwa ne kawai da duwatsu na saka. Ina yi ne domin yara su yi zaton akwai abinci su daina kuka su kwanta."
Wannan maganar ta sosa wa Umar (RA) rai matuƙa har sai da ya fashe da kuka.
Ba ta san cewa shi ne Amirul Mu’minin ba. Sai ta ƙara cewa:
"Allah zai hukunta Umar, domin bai san halin da muke ciki ba!"
Sai Sayyidina Umar da wanda suke tare da shi s**a koma baitul mali (ma’ajiyar gwamnati), Umar ya ɗauko buhun hatsi, mai, nama da zuma da kansa, ya ɗora a bayansa.
Wanda suke tare da Umar ya roƙe shi ya bar shi ya ɗauka, amma Umar ya ce:
"Shin kai zaka ɗauki zunubin Umar a ranar kiyama?"
Sai s**a dawo gidan matar. Umar ya girka abincin da kansa, ya zuba wa yara s**a ci har s**a koshi, s**a yi dariya s**a kwanta. Matar ta ce masa:
"Zan so ace Umar ya zama kamar kai"
Bata san Shine Umar din ba.
Wallahu a'alam.
✍️✍️ Yunusa Magaji Bala Gombe