Yahya Ahmad

Yahya Ahmad Striving for Jannah
Sunnah lover

soon
13/01/2026

soon

17/11/2025

صديقي المميز! تلاوتك في المسابقة أدهشتني كثيرًا. أفتخر بك أكثر مما أستطيع أن أعبّر. أسأل الله أن يزيدك فهماً وبصيرة.

28/08/2025

من يعاني من الضيق يدعي ...

اللَّهُم إنّي أودعتُك قلبي المثقل، وفوّضت إليك أمري كلّه، فطهِّر صدري من الضيق، وامسح عن روحي غبار الهمّ، واغمرني بسكينةٍ من عندك تشرح الصدر وتُقوّي العزم، واجعلني من عبادك الذين نادوك فأجبتهم، ورجوك فأكرمتهم.

28/08/2025
KASAYA KA KARANTA ZAKAYI FARIN CIKI ZAKAJI DADI, DAKA SAMU SAUKI CIKIN RAYUWAR KA.Dan Allah Ka tai Maka Ka Karanta sanna...
18/08/2025

KASAYA KA KARANTA ZAKAYI FARIN CIKI ZAKAJI DADI, DAKA SAMU SAUKI CIKIN RAYUWAR KA.

Dan Allah Ka tai Maka Ka Karanta sannan Kuma Kayi Sharing Dan Yan Uwa Su Anfana Kai ma Kayi Sadakatul Jariya Lada Mai Gudana.

Akwai wasu Ibadun Guda Shiadai (6) Annabi Sallallahu Alaihi Wa Sallam yace wannan Ibadun Girmar Sa basu da Iyaka Falalar Sa Basu da Karshe. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam yace duk Wanda ya Lizamci wannar Ibadun ya Rabauta Duniya da Lahira.

***Na Farko Shine Kamar Haka (1)
Rak'atul Fajiri, Raka'a Biyu kafin Sallar Asbahi, Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam yace Rak'atul Fajiri yafi Duniya da abinda ke cikin ta.

*** Na biyu Shine Kamar Haka (2).
Duk Wanda yake Karanta Ayatul Kursiyu a ko wace Sallah Babu abun da zai hanashi Shigan Aljannah sai dai in bai mutu bah.

*** Na uku shine kamar haka (3).
Sallar Witiri.

*** Na hudu shine kamar haka (4).
Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam yace.
Duk Wanda yace Subhanallahi Wabi Hamdihi sau 100 Allah zai gafarta masa zununban SA Koda sun Kai Kunfar kogi ne .

***Na Biyar shine kamar haka (5)
Duk Wanda ya kara ta suratul Iklasi sau 10 Allah zai Gida masa bene a Aljannah (Suratul Iklas) Kulhuwa Kenan

***Na shida shine kamar haka (6)
Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam yace shin bazan Maka nuni zuwa ga Taskar Aljannah bah sai yace eh ina so ya RASULULLAH kamin nuni .

Sai yace Fadan Lahaula Wala kuwata Illa Billah .

Wannar Ibadah Guda Shaidan Nan karkayi Wasa dashi Allah mana Jagora.

Dan Allah Ka Daure kayi sharing Dan Yan Uwa Su Anfana Kai ma Kayi sadakatul Jariya.

Prof Muhammad Sani Umar Rijiyar Ilmi ❤️.
Salihi Ahmad Ibrahim ✍️

MULKIN ADALCI Manzon Allah SAW Yace" Ba Cuta Ba Cutarwa" A lokacin Khalifancin Sayyadina Umar bn Khattab (RA), ya kasanc...
16/08/2025

MULKIN ADALCI Manzon Allah SAW Yace" Ba Cuta Ba Cutarwa" A lokacin Khalifancin Sayyadina Umar bn Khattab (RA), ya kasance yana yawo tsakiyar dare a cikin garin Madina domin ganin halin da jama'ar Madina ke ciki.

Sai Wata rana suna cikin zagaya garin Madina sai s**a ji ƙarar yara suna kuka a cikin wani gida.

Sayyidina Umar (RA) ya matsa kusa da gidan, ya nemi izini shiga gidan domin ya duba abin da ke faruwa.

Sayyidina Sai ya tarar da wata mata ta dora tukunya a kan wuta, yayin da yaranta ke kuka suna jiran abinci. Sai Khalifa Umar ya tambaye ta:

"Me k**e dafa wa haka, kuma me yasa yara ke kuka?"

Sai matar ta ce:

"Babu abinci a cikin tukunyar, ruwa ne kawai da duwatsu na saka. Ina yi ne domin yara su yi zaton akwai abinci su daina kuka su kwanta."

Wannan maganar ta sosa wa Umar (RA) rai matuƙa har sai da ya fashe da kuka.

Ba ta san cewa shi ne Amirul Mu’minin ba. Sai ta ƙara cewa:

"Allah zai hukunta Umar, domin bai san halin da muke ciki ba!"

Sai Sayyidina Umar da wanda suke tare da shi s**a koma baitul mali (ma’ajiyar gwamnati), Umar ya ɗauko buhun hatsi, mai, nama da zuma da kansa, ya ɗora a bayansa.

Wanda suke tare da Umar ya roƙe shi ya bar shi ya ɗauka, amma Umar ya ce:
"Shin kai zaka ɗauki zunubin Umar a ranar kiyama?"

Sai s**a dawo gidan matar. Umar ya girka abincin da kansa, ya zuba wa yara s**a ci har s**a koshi, s**a yi dariya s**a kwanta. Matar ta ce masa:

"Zan so ace Umar ya zama kamar kai"

Bata san Shine Umar din ba.

Wallahu a'alam.

✍️✍️ Yunusa Magaji Bala Gombe

Kiyi WankankiKi Saka Hijab ƊinkiKi Sanya Niqab ƊinkiKiyi Fitarda Zata Kare MutuncinkiKibar Kula Masu KushekiKarki Damu D...
12/08/2025

Kiyi Wankanki
Ki Saka Hijab Ɗinki
Ki Sanya Niqab Ɗinki
Kiyi Fitarda Zata Kare Mutuncinki
Kibar Kula Masu Kusheki
Karki Damu Da Masu Zaginki
Kiyi Ɗa'a Ga Ubangijinki
Ki Nemi Yardar Mahaliccinki
Karki Biyewa Son Ranki
Indai Kin Riƙe Mutuncinki
To A Lahira Zakiji Daɗinki
Gidan Aljannah Shine Ɗakinki

Muje maha
12/08/2025

Muje maha

ABUBUWA GUDA 10 DA SHIRKA KE GADARWA MAI YINTA1. ZUBAR DA DUKKAN AYUKAN ALHERIAllah baya karɓar ibada daga mai shirka.Da...
12/08/2025

ABUBUWA GUDA 10 DA SHIRKA KE GADARWA MAI YINTA

1. ZUBAR DA DUKKAN AYUKAN ALHERI

Allah baya karɓar ibada daga mai shirka.
Dalili: "Da sun yi shirki, to abin da s**a aikata ya bace." (Suratul An’am: 88)

2. HARAMTAWA SHIGA ALJANNA

Mai shirka ba zai shiga Aljanna ba idan bai tuba kafin ya mutu.
Dalili: "Lalle wanda ya yi wa Allah shirka, to Allah ya haramta masa Aljanna." (Suratun Ma’idah: 72)

3. SHIGA CIKIN WUTA

Hukuncinsa shi ne wuta mai zafi har abada (idan bai tuba ba).
Dalili: Suratun Ma’idah: 72.

4. ZAMA ABOKIN SHAIDAN

Mai shirka yana cikin abokan shaidan a duniya da lahira.

5. FADUWAR MARTABA A WAJEN ALLAH

Bai da wata daraja a wajen Allah sai dai wulakanci.
Dalili: Suratul Hajj: 31.

6. TSANANTAR AZABA A LAHIRA

Mai shirka zai sha wahala fiye da kafirai waɗanda ba su san gaskiya ba.
Dalili: Suratun Fussilat: 27.

7. ZAMA MAFI GIRMAN ZALUNCI

Shirki shi ne mafi girman zalunci saboda ya tauye hakkokin Allah.
Dalili: "Lalle shirki zalunci ne mai girma." (Suratul Luqman: 13)

8. RASHIN AMINCEWA DAGA ALLAH

Allah baya taimakon mai shirka a lahira.
Dalili: Suratul Hajj: 22.

9. RASHIN SAMUN GAFARA IDAN YA MUTU A KAI

Idan mutum ya mutu a kan shirki ba tare da tuba ba, Allah ba zai gafarta masa ba.
Dalili: "Lalle Allah baya gafarta a yi masa shirka." (Suratun Nisa’: 48)

10. ZAMA CIKIN HASARAR DUNIYA DA LAHIRA

Mai shirka ya yi hasarar duniya da lahira gaba ɗaya.
Dalili: Suratul Hajj: 11.

Fadakarwa:
Duk yadda zaayi kada ka yarda ka aikata shirka kayi iya kokarin domin ka mutu akan tauhidi

Kada ka yadda ka mutu mushriki

ALLAH ka azirtamu da mutuwa akan tauhidi da tsaftatacciyar Aqeeda

Nigeria kasarmu ta gado
11/08/2025

Nigeria kasarmu ta gado

MANYAN ALAMOMIN SON MANZON ALLAH ﷺ1. BIN SA KAI TSAKANIN HALA DA HARAMDalili: Allah ya ce:"Ku bi Allah, ku bi ManzonSa.....
08/08/2025

MANYAN ALAMOMIN SON MANZON ALLAH ﷺ

1. BIN SA KAI TSAKANIN HALA DA HARAM
Dalili: Allah ya ce:

"Ku bi Allah, ku bi ManzonSa..." (Surat An-Nisa: 59)

Ana nuna kaunar Manzon Allah ta hanyar bin umarninsa da nisantar haram.

2. YAWAN AMBATO DA SALATI A KANSA

Dalili: Annabi ﷺ ya ce:

"Duk wanda ya yi mini salati sau ɗaya, Allah zai yi masa salati sau goma." (Muslim)

Yawan salati yana nuna kauna da biyayya.

3. KISHIN MUSULUNCI DA AIKIN SUNNARSA

Dalili: Annabi ﷺ ya ce:

"Duk wanda ya raya sunnata, yana sona, kuma wanda ya sona zai kasance tare da ni a Aljanna." (Tirmidhi)

4. YAWAN KARANTA SIRARSA DA HADISANSA

Dalili: Allah ya ce:

"Lallai a cikin Manzon Allah akwai abin koyi mai kyau." (Al-Ahzab: 21)

5. NISANTAR SABAWA ANNABI ﷺ

Dalili: Allah ya yi gargadi:

"To, waɗanda s**a saba masa, su ji tsoron fitina ko azaba mai raɗaɗi." (An-Nur: 63)

6. SON DUK WANDA YA BIYAYYA MASA

Dalili: Annabi ﷺ ya ce:

"Al’amal mafi soyuwa a wurin Allah shi ne kauna saboda Allah da ƙi saboda Allah." (Abu Dawud)

7. YIN KAMARSHI A HALI DA ZUZZURFA

Dalili: Annabi ﷺ ya ce:

"Ku yi koyi da ni a cikin yadda nake yin salla." (Bukhari)

8. FADAKARWA DA KIRA ZUWA GASKIYA

Dalili: Allah ya ce:

"Ka yi kira zuwa hanyar Ubangijinka da hikima..." (An-Nahl: 125)

9. TUNA DA SHAN WAHALOLINSA

Dalili: Annabi ﷺ ya sha wahala domin isar da sakon Allah, kuma tunawa da hakan yana ƙara kauna.

10. FATAN HADUWA DA SHI A ALJANNA

Dalili: Annabi ﷺ ya ce:

"Mutum zai kasance tare da wanda yake so." (Bukhari da Muslim)

اللهم صل و سلم على نبينا محمد

Abu Ja'afar Assunny ✍️

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Yahya Ahmad posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share