31/03/2026
⚠️ BA NA CIKA RUBUTU A SOCIAL MEDIA BA… AMMA YAU DOLE NE ⚠️
Nigeria na cikin wani hali mai tayar da hankali, musamman a Arewa. Akwai wasu da ke ƙoƙarin raba ƙasa gida biyu ta fuskar addini da yare… kuma wannan ba sabon abu bane—an daɗe ana shirya shi.
Abin takaici, wasu daga cikin ‘yan siyasa ba su damu da makomar al’umma ba. Abin da ya dame su kawai shine: “Me zan samu?”
Mu kuma muna ta kallon abin yana faruwa… mun manta da kare asalinmu, mun koma tunanin abin da za mu ci yau kawai.
Ku tuna: mutane ne za ku jagoranta, ba aljannu ba. Idan zaman lafiya ya lalace, me zai rage?
👉 Lokaci ya yi da za mu farka. Mu tashi mu kare kanmu da makomarmu.✍️