25/07/2022
TARKON MUTUWA 1
Complete book
Typing Suleiman Zidane kd.
Whatsapp
BOOK ONE
A wani zamani can baya mai tsawo da ya shude a lokacin da ake yin kashin dankali wato Babba a sama, Kanana a kasa. Ma'ana mai karfi, basarake da attajirai suke cin karan su ba babbaka.
A wannan lokaci zalunci ya yawaita, sam babu adalci, doka bata aiki sai akan talaka, mara karfi da makaskanci.
A daidai wannan zamani ne akayi wata nahiya wacce ta shahara a duniya a harkokin kasuwanci, Karfin mulki da yawan al'umma. Kasar da tafi dukkannin kasashen dake nahiyar daukaka itace Bindal.
Duk wani dan kasuwa dake mu'amala acikin birnin Bindal indai yana son ya tsira da mutincinsa da kuma dukiyarsa to dole yakasan ce dole ribar da ya samu a kullum ya rabata gida uku.
Kaso daya shine naka kaso biyu kuma sai ya kaiwa sarki Shamssal.
Sarki Shamsal ya kasance gawurtaccen jarumi mashahurin mayaki wanda babu kamarsa a nahiyar gaba daya domin a tarihin jarumtakarsa ba'a taba kai shi kasa ba a filin daga kuma ba'a taba yi masa rauni ba a yaki ko a gasar jarumtaka.
Yana iya shafe sa'a goma sha biyu yana yaki ba tare da gaji ba kuma yana iya yin tafiyar kwana bakwai a kasa cikin yin gudu ba tare da ya tsaya ko don ya huta ba sai dai kawai ya daga battar ruwa yasha yana cikin gudun.
Kai idon Sarki Shamsal yayi wani abun jarumtaka sai kaga kamar ba mutum bane ba shi, aljanine komai yawan rundunar mayaka yana iya tarwatsa su ya kashe na kashewa, MASU GUDU SU GUDU don tsira da rayuwar su.
A bangaren zalin ci kuwa masu hasashe sun tabbatar da cewa babu wani Sarki a nahiyar kaf wanda yafi Sarki Shamsal domin shi 'yan uwan sama sarakai cin zalinsu yake yi bare talaka.
Idan ya kyallara ido yaga wani Sarki da kyakykyawar mata sai dai kawai ya aika masa sakon ya kawota da kansa, Idan Sarkin yaki kawo ta zai iya rasa ransa ko mulkinsa don haka yana rawar jiki zai kai ta .
Batun haraji a kan talakwa babu inda aka tsanantashi sama da birnin Bidal ko yaya talaka ya yi laifi yanzunnan sai a zaneshi ko kuma a kai shi kurkuku a yanke masa shekara biyu ko fi,
A ta kaice dai in ban da Sarki Shamsal da fadawansa da kuma ya yan baran darsa da masu yi masa biyayya babu mai kwanciyar hankali a cikin birnin BINDAL.
A can karshen birnin Bindal a bangaren kudu a kwai wani makeri wanda ake kira da suna Satyan
Makeri satyan tsoho ne tukuf domin shekarun sa sunkai dari da biyar kuma tun baifi shekara tara ba a duniya ya kware a harkar kira kuma ya shahara domin gadon sana'ar yayi yana shekara taran mahaifinsa ya rasu kuma yaci gaba da aiwatar da aikin mahaifin nasa Hatta makaman yakin gidan Sarki Shamsal a makerar Satyan ake kerasu ba a taba samun wani sabani ba tsakaninsa da gidan Sarki Shamsal bai taba ganin tsoho satyan ba haka shima tsoho satyan bai taba ganin saba
A karkashin tsoho satyan akwai yara ma'aikata kimanin su saba'in da daya kuma duk suna samun abin da suke rayuwarsu a karkashinsaAlbarkacin kayan yakin da yake kerawa masarautar ne yasa ba' tsananta masa haraji ba,
kuma tun a zamanin mahaifin Sarki Shamsal hakaabin yake wakekana.
Tshoho satyan yana matar aure guda daya wacce itama girma ya kamata domin shekarunta sun kai
saba'in.
Allah ya albarkacesu da 'ya 'ya biyu kacal a duniy,
mace da namiji macen itace babba kuma shekarun ta sun kai ashirin da biyar,
Ana kiranta da suna Sadirat.
Sadirat kyakykyawa dai dai gwargwado mai kyan siffa ta taso da farin jini sosai a wajen samari
amma saboda itace kadai ke taimakon mahaifiyarta a ayyukan gida bata son ta yi aure har sai kaninta Hatyan yayi saboda
Matarshi za ta zauna a gidan ta rinka tai makon mahaifiyarsu,
ita kuwa dauketa za ai akaita wani gida.
Tsakanin sadirat da hatyan bambancin shekaru Hudu ne wato a yanzu Hatyan yana da shekaru Ashirin da daya kacal a duniya.
Allah daya gari bambam , ko kadan Hatyan bai gaji harkar kira ba.
Tunda ya taso da kuruciyarsa babu abinda yake so sama da harkar farauta don haka kusan kullum da koyaushe yana cikin daji,
Tun safe idan ya fita farauta baya dawowa sai rana ta fadi.
Wani ikon Allah kuma sai ya zamana cewa yana da nasibi matuka a harkar domin bai taba fita farauta ya dawo ba wani abu ba sai anganshi ya kamo babbar dabba ko wani babban tsuntsu,
Tun Hatyan na da shekara tara a duniya aka gane cewa sadauki ne domin tun a sannan yake iya gumurzu da manyan dabbobin daji kuma ya kashesu da hannunsa,
Wannan baiwa da Allah ya bashine tasa shi kansa Sarkin farauta na Birnin ya jashi a jikinsa
ya kaunace shi ainun hakannema ya rinka taimaka masa da yansim kan daji dana tsafi domin samun tsari.
A kullum abin da Sarkin mafarautar ke nunawa Hatyan shine lallai ya boye jarumtakarsa kada mutanen gari su sani saboda al'adar Sarki Shamsal itace dayaji ance wani sadauki ya taso a birnin sa saiya tura a sirrance a kasheshi .
Bakomai ne ya janyo hakan ba face bokayaensa sun gaya mashi cewa duk ranar da aka sami gagarumin sadauki mai irin baiwarsa ta jarumtaka da juriyar yaki da gudu a birnin to shine zai
karbi mulkinsa.
Domin cigaba shiga nanππ
Tarkon Mutuwa Hausa novel