19/05/2026
INDA DAYA DAGA CIKIN WADANNAN ABUBUWAN A HANNUN MUTANE YAKE... DA YANZU 80% NA MUTANE BASA RAYE.
Mutum yana da rauni, kuma zuciyarsa cike take da son kai, kishi, da hassada a boye. Da a ce Allah ya bada ikon wadannan abubuwan a hannun dan Adam... da tuni duniya ta zama wani guri mai matukar ban tsoro.
1. Mutuwa
Da makiyinka zai sa a dauki ranka tun kafin ka gane wane ne shi ainihi. Da ba a barin wanda ake hassada da shi ya kara ko kwana daya a raye.
2. Lafiya
Da an bar ka a kwance kana ihu da neman dauki har ka mutu. Saboda a gaskiyar magana, wasu mutanen... jinyarka ne farin cikinsu.
3. Ciyarwa
Da sai ka zama bawan wani, kana ta rusunawa kafin a baka abinda zaka sa a bakinka. Da wanda aka tsana... yunwa ce zata kashe shi.
4. Rufe Asiri
Da babu wanda zai iya sake fita a cikin mutane. Mutum bai iya ganin aibin wani ya rufe. Da tuni an yaye mayafin kowa.
5. Daukaka
Da babu wani dan talaka ko wanda ba kowa ba da zai taba zama wani abu a rayuwa. Da an toshe masa duk wata kofa ta nasara tun kafin ya fara tafiya.
6. Gafara
Mutum ko yace ya yafe maka, a bakinsa ne kawai... a zuciyarsa baya taba mantawa kuma zai jira ranar ramako. Da a ce shiga Aljanna ta danganta da gafarar mutane ne, da kowa a wuta zai kare.
7. Numfashi
Da har iskar da muke shaka sai an sa mata farashi. Da masu kudi ne kadai zasu rika shakar iska a duniya... wanda bashi da kudin biya, zai mutu a tsaye a gaban iyalansa.
Babban abin farin ciki a nan shine...
Mahaliccinmu yasan duhu da muguntar da ke boye a cikin zuciyar mutum. Shiyasa ya rike makullin wadannan abubuwan a hannunSa kadai.
Duk girman kiyayyar mutum a kanka... ba zai iya taba ko daya daga cikin wadannan ba.
Don haka, ka kwantar da hankalinka.
# #